Revelation of John 2

1‘’Zuwa ga mala’ikan dake ikilisiyar Afisus, ka rubuta: ‘Wadannan sune kalmomin wanda ke rike da taurari bakwai a cikin hannun damarsa. wanda yake tafiya a tsakanin zankayen fitilun zinari bakwai, 2‘’Na san abubuwan da ka yi, da famar ka, da hakurinka da jimirinka. Na sani ba ka jimrewa miyagun mutane, na sani ka gwada wadanda suka ce da kansu, su manzanni ne, amma ba haka ba, ka tarar da su makaryata.

3Na san kana da tsawon jimrewa, kuma ka sha wahala sosai sabili da sunana, kuma baka gaji ba. 4Amma ga rashin jin dadi na da kai, ka bar kaunar ka ta fari. 5Domin haka ka tuna daga inda ka fadi. Ka tuba ka yi abubuwan da ka yi da fari. Sai fa ka tuba, zan zo maka in kuma cire fitilar ka daga mazauninta.

6Amma kana da wannan: Ka tsani abubuwan da Nikolatawa suka yi, wanda nima na tsana. 7wanda yake da kunnen ji ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bashi dama ya ci daga itacen rai, wanda ke cikin firdausin Allah.“”

8Zuwa ga mala’ikan da ke Ikilisiliyar Samirna rubuta: ‘Wadannan su ne kalmomin wanda yake shine farko shine karshe, wanda ya mutu ya sake rayuwa kuma. 9‘’Na san wahalun ka da talaucin ka amma kana da arziki. Nasan masu bata suna wadanda suke cewa su Yahudawa ne, amma ba haka suke ba. Su majami’ar Shaidan ne.

10Kada ka ji tsoron wahalar da zaka fuskanta nan gaba. Duba! Shaidan yana gab da jefa wadansun ku cikin kurkuku, domin a gwada ku, kuma zaku sha wahala ta kwana goma. Kuyi aminci har ga mutuwa zan baku rawanin rai. 11wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Shi wanda yayi nasara ba zai cutu a mutuwa ta biyu ba.“”

12‘’Zuwa ga mala’ikan dake ikilisiyar Burgamas rubuta: ‘Wadannan ne kalmomin wanda ya ke da takobi mai kaifi biyu; 13‘’Na san inda kake zama can inda kursiyin shaidan yake. Duk da haka ka rike sunana da karfi, na sani baka yi musun bangaskiyar ka da ni ba, ko a lokacin Antifas mashaidina, amintaccena, wanda aka kashe a tsakaninku, can inda shaidan yake zama.

14Amma ga rashin jin dadi na kadan da kai: Kana da wadansu da suke rike da koyarwar Bil’amu kamkam, wanda ya koya wa Balak ya sa abin tuntubi gaban ‘ya’yan Isra’ila, domin su ci abincin da aka mika wa gumaka kuma suyi fasikanci. 15Hakannan kuma wasunku sun rike koyarwar Nikolatawa kamkam.

16Sabili da haka ka tuba! Idan ka ki zan zo gare ka da sauri, kuma in yi yaki gaba da su da takobi dake cikin bakina. 17Bari wanda yake da kunne ya sauriri abin da Ruhu yake fadawa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bada wata boyayyar manna, kuma zan bashi farin dutse da sabon suna a rubuce a kan dutsen, suna wanda ba wanda ya sani, sai shi wanda ya karbe shi.“”

18Zuwa ga mala’ikan ikilisiyar Tiyatira rubuta: ‘Wadannan sune kalamomin Dan Allah, wanda yake da idanu kamar harshen wuta; sawayen kamar gogaggiyar tagulla: 19‘’Na san abin da ka yi, kaunar ka, da bangaskiya da hidima da tsawon jimrewar ka. Na san abinda ka yi bada dadewa ba ya fi abinda ka yi da fari.

20Amma ga rashin jin dadi na da kai: Kana hakurce wa matar nan Yezebel, wadda take kiran kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta, ta rudi bayina suyi fasikanci kuma su ci abincin da aka mika wa gumaka sadaka. 21Na bata lokaci domin ta tuba amma bata so ta tuba da fasikancin ta.

22Duba! zan jefa ta a kan gadon jinya, wadanda kuma suka yi zina da ita za su shiga babbar wahala, sai dai in sun tuba daga ayukan ta. 23Zan buga ‘ya’yanta da mutuwa, kuma dukan ikilisiyoyi zasu san cewa nine wanda nake bincike tunani da zukata. Zan ba kowanen ku bisa ga ayyukansa.

24Amma ga sauran ku dake cikin Tayatira, ga kowanen ku wanda bai rike wannan koyarwar ba, kuma bai san abinda wadansu suke kira zurfafan abubuwan Shaidan ba--ga ku na ce ban sa muku wata nawaya ba.’ 25Duk da haka dole ku tsaya da karfi har in zo.

26Wanda yayi nasara da wanda ya yi abin da na yi har karshe, a gareshi zan bada iko akan al’ummai 27Zai yi mulkin su da sandar karfe, zai farfasa su kamar randunan yumbu.” 28Kamar yadda na karba daga wurin Ubana, ni kuma zan bashi tauraron asubahi. Bari wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fadawa ikilisiyioyi.“”

29

Copyright information for HauULB